RAMADAN KARIM: 27-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Litinin, Allah ya nuna mana rana ta 27 a Ramadan. Yau ma ga nasiharmu:
A yau za mu yi tsokaci ne game da wani mummunan al’amari, wanda yake kassara al’ummarmu. Wannan lamari kuwa shi ne zalunci. Babu shakka, a duk lokacin da ka ga lamurra sun lalace, to zalunci shi ne sila. Lallai ne mu kiyayi aikata zalunci. Mu riƙe adalci, shi ne babban jigon inganta rayuwa.
Allah ya la’anci azzalumai kuma ya haramta zalunci. A cikin Alƙur’ani mai girma, Suratu Shura 42:42, ya ce: “La’ana ga azzalumai.” Haka kuma Manzon Allah (saw) a Hadisin Imam Bukhari mai lamba 2447 da Imam Muslim, Hadisi mai lamba 2578, ya ce: “Ku ji tsoron zalunci…”
Ya Allah, muna roƙon ka, ka kiyaye mu daga zalunci. Ka ba mu ikon yin adalci ga kawunanmu da sauran al’umma a kowane lokaci. Amin.
__________













