RAMADAN KARIM: 12-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Bayan haka, a yau Lahadi, Allah ya nuna mana rana ta 12 a Ramadan. Yau ma ga ‘yar nasiha:
A yau nasiharmu, kira ne da jan hankali zuwa ga mawadata dangane da falalar ciyarwa. Babu shakka muna da ɗinbim mabuƙata a ko’ina ka duba. Mu daure mu riƙa taimakawa, domin samun ijararmu daga Allah mai girma.
Allah a cikin Suratul Baƙarah 2:261, yana cewa: “Misalin waɗanda suke ciyar da dukiyoyinsu a tafarkin Allah kamar misalin ƙwayar hatsi ce wadda ta tsiro, ta fitar da zangarniya bakwai, a kowace zangarniya akwai ƙwayoyi ɗari. Allah yana ninka lada ga wanda ya so kuma Allah mai yalwar baiwa ne, masani.”
Annabi Muhammadu (saw), a Hadisin Bukhari na 1419, yana cewa: “Duk wanda ya yi sadaka da abin da ya samu na halal (kuma Allah ba ya karɓar sai halal), to Allah zai karɓe ta da hannun damansa, sannan ya raine ta (ya bunƙasa ta) ga mai ita kamar yadda ɗayanku yake rainon ɗan dokinsa, har ta zama kamar dutse mai girma.
Muna roƙon Allah ya huwace mana abin ciyarwa kuma ya ba mu ikon ciyarwa saboda shi. Amin-Summa-Amin!
__________













